Free Web Hosting Provider - Web Hosting - E-commerce - High Speed Internet - Free Web Page
Search the Web

Mujahidah

Babu Hukuma Sai ta Allah      -       Malam Zakzaky

     Fitowa ta 12                                     Jimada Thani 1421
 
Abubuwan ciki:
Fitowa ta 12
  Jimada Thani
 DAGA TEBURIN EDITA
Irin Wainar da muka toya
 SHARHIN MUJAHIDAH
A gaida 'yan uwa mata
 WASIKU
Wasiku uku daga 'yan uwa mata
 BABBAN LABARI
Taron Nasarar Hizbullah a Zariya

Hizbullah ba za ta taba daukan kaskanci ba

Dole ne Malamai su hada kansu

Wajibi ne mu zama abin koyi

 HIRA TA MUSAMMAN
Shawara ga iyayen da za su tura 'yayansu Jami'a

Da'awarmu na samun karbuwa a wajen dalibai

Mace mai tsoron Allah ya kamata ta je Jami'a

 LABARI
Lalacewar mata a Nijeriya

 FADAKARWA
Aikin da ke gaban 'yan uwa mata
 NASIHA
Rayuwar aure a Musulunci

Kishiya Ko Abokiyar Zama?

 YARA
Ka tausaya ma dabbobi
 LIKITA
Toshewar fitowar jariri da tsawaitar nakuda
 TARIHI
Gwarzantakar Ummu Wahab(R.A)
 RAYUWA
Muhimmancin soyayya a rayuwar aure

Shirin hana almajirai bara zai yi nasara kuwa?

Hattara 'yayan talakawa

Kikan duba shafin

Almizan
  kuwa?
The Witness
  kuma fa?
Daga Teburin Edita
Wainar da muka toya

Bismillahir rahmanir rahim

Kafin in labarta maku irin wainar da muka toya a wannan fitowa ta 12, dole in ba ku hakuri kan jinkirin da aka samu. Babban dalili shi ne Hukumar gudanarwarmu ta mai da hankalinta sosai ga mallakar sabbin kwamfuta da sauran kayan aiki, abin da zai sa insha Allah mu ci gaba da fitowa ba kakkautawa.

Wainar da muka toya tana da yawa, don haka ba zan iya lissafo su ba. Amma dai mafi girmansu ita ce labarin abubuwan da suka wakana a taron da 'yan uwa mata suka shirya na murnar nasarar da kungiyar Hizbullah ta Lebanon ta samu kan Yahudawa 'yan kaka-gida a Lebanon. Kai wannan kokari na 'yan uwa mata abin alfahari ne, ko ba komai shi ne na farko a wannan harka Islamiyya, a inda aka gayyato Shehunnan Malamai daga makarantu biyu na addinin Islama-Shi'a da Sunni. Wakilinmu Yusuf Abdullah ya dauko mana komai. Ya kawo jawabin Shaikh Ali da Shaikh Mahir, da Shaikh Zakzaky da na Farfesa Ahmad Khani. Kai abin dai sai kun karanta.

Wata wainar kuma ita ce hirarrakin da Wakilanmu suka yi da Jami'an kungiyar dalibai musulmi (MSS) na Jami'o'in Ahmadu Bello Zariya, Jami'ar Bayero Kano, Jami'ar Usman Danfodiyo Sakkwato da Kwalejin Kimiyya da fasaha ta Kaduna. Ba mu gina wani labari kwara daya kan abubuwan da suka ce ba don mai karatu ya tsinkayo darussan da ke cikin hirarrakin da kansa. Wannan babbar nasara ce ga mujallar nan, domin za ta sami shiga a wadannan wurare da muke matukar son mu jawo su a jika. Don haka ina labarta wa 'yan wadannan manyan makarantu cewa wannan mujalla tasu ce, kuma tana sa ran ganin rubuce-rubuce daga gare su.

Hmn aka ce wai kishi kumallon mata. Ina ga ba haka bane. In mutum ya karanta makalarmu kan haka na tabbata zai gamsu. Waina ta uku kenan.

Wainarmu ta hudu ita ce maganar bara da ake kokarin a kau da ita a Arewacin Nijeriya. Wannan matsala ce da ta yi katutu a kasar nan. Labarinmu kan Wakilan da Hajiya Asma'u, matar Gwamna Makarfi na Jihar Kaduna ne ta tura Zariya karkashin Hajiya Sa'adatu Sani.

Sai kuma wainar da ya kamata in ambata a karshe ita ce wacce Isah Khamis ya rubuta, inda yake gargadi ga 'ya'yan talakawa. Allah ya sa mu amfana. Sauran wainar sai an duba ciki a gan su.

A ci ko a karanta lafiya zan ce?

   

Komawa Babban shafinmu