| Ka girmama dabbobi
Daga Husaini Tahir Samaru
Wata rana Imam Hasan, alaihis-salam yana cikin cin abinci, sai kare ya zo ya tsaya gabansa, yana kallon sa. Imam Hasan (AS) ya sanya loman abinci a bakinsa ya kuma jefa ma kare nasa a gabansa. Ya ci ya kada jelarsa don godiya, ya yi haushi ya daga kansa ya kalli Imam Hasan (AS).
Imam Hasan (AS) ya jefa wani loman abinci a gaban karen. Wani mutum wanda zai wuce ta wurin ya zo gaba ga Imam ya ce, "Ba daidai bane wannan kare ya tsaya a gabanka ya hana ka cin abinci cikin natsuwa, ka yi mani izini sai in buge shi in korai." Sai Imam Hasan (AS) ya ce masa "A'a kar kai haka. Allah da ya halicce shi dabba yana son shi. Ai yunwa ce. Zan ji kunya gaban Allah in ci abincinsa da albarkansa sannan in ki bai wa halittarsa, duk da yana jin yunwa yana kallo na."
An fassaro daga Children guide to Islam na Hujjatul Islam Ibrahim Amini.
|